Ana sa ran a ranar Asabar, sanatoci a majalisar dattawan Amurka za su saurari muhawarar karshe kan shari’ar tsige tsohon shugaba Donald Trump.
Mafi yawan ‘yan Republican a majalisar dattawan Amurka sun kada kuri’a jiya Talata game da kin amincewa da gudanar da shari’ar tsige tsohon shugaba Donald Trump.
Ana shirin rantsar da ‘yan Majalisar Dattawan Amurka a matsayin alkalai da kuma masu taimaka musu a shari’ar tsige tsohon shugaban kasa Donald Trump.
An rantsar da Dan Jam’iyyar Democrat Joe Biden, a yau Laraba a matsayin shugaban Amurka na 46 a Majalisar Amurka.
Ku kalli Shan Rantsuwar Joseph R. Biden da Kamala D. Harris da Za’a yi a Washington. Ranar Laraba 20 ga Watan Janairu Daga Karfe 11:30 na Safe Agogon Washington DC
Hukumomi a Amurka sun tsaurara matakan tsaro a birnin Washington DC yayin da ya rage kwanaki a rantsar da zababben Shugaba Joe Biden a matsayin shugaban Amurka na 46.
Zababbaen shugaban Amurka Joe Biden ya ce “a gwagwarmayar kare Amurka, Dimokradiyya ta yi nasara,” a jawabin da yayi ranar Litinin, jim kadan bayan da wakilai na musamman suka tabbatar da zaben sa a matsayin shugaban kasa.shugabancinsa.
Wannan na zuwa ne yayin da Joe Biden ya damka wa mata sashen sadarwar fadar White House
Zababben shugaban Amurka, Joe Biden da Mataimakiyar Shugaban mai jiran gado Kamala Harris, sun sanar da nadin tawagar mata zalla a fannin sadarwa.
Hukumar da ke hidima ga cibiyoyin gwamnatin tarayyar Amurka (GSA a takaice), ta tabbatar cewa zababben shugaban kasa Joe Biden, shi ne a ta bakinta, “wanda, ga alama ya yi nasara” a zaben ranar 3 ga watan Nuwamba.
Masu zanga zanga sun yi taro a Washington a jiya Asabar domin nuna goyon baya ga shugaba Donald Trump da zargin da ya yake yi na tabka magudi a zaben ranar 3 ga watan Nuwamba da babu hujja.
Jiya Lahadi, a karon farko, Shugaban Amurka Donald Trump ya nuna ya amince da cewa dan takarar Demokrat Joe Biden "ya lashe" zaben shugaban kasa kusan makonni biyu da suka gabata, amma sanadiyyar magudi.
Domin Kari
No media source currently available
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa
Hukumomi a Najeriya sun daura damarar yaki da magudin zabe, a wani muhimmin lamari ga dimukradiyya a Afirka. Bayan babban zaben 2023, Najeriya ta fara daukan matakan hukunta wadanda aka samu da laifin magudin zabe domin dawo da martabar tsarin zabe a kasar.
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.