Shugaba Bola Tinubu ya bukaci Babban Bankin Najeriya da ya dakatar da aiwatar da dokar haraji ta yanar gizo da ya dora kan 'yan kasa wacce aka fi sani da cybersecurity levy, sannan ya bayar da umurnin a sake nazarin matakin.
Ododo ya bayyana hakan ne yayin da ya kai ziyarar ganewa idonsa jami’ar ta Confluence University a ranar Asabar.
Kwana biyu bayan kaddamar da katin lamuni na kudin dala a Najeriya, wato American Express Credit Card, irinsa na farko a Afrika, masana tattalin arziki sun fayyace bambancinsa da kudin Crypto, yayin da masu masana’antu ke cewa, akwai bukatar wayar da kan ‘yan kasuwa akan alfanun aiki da katin.
A ranar 23 ga watan Afrilun daya gabata ne, kotun ta umarci Hukumar EFCC ta mikawa tsohon gwamnan takardar sammaci ta hannun lauyansa game da tuhume-tuhumen halasta kudaden haram da ake yi masa.
Kudirin dai ya samu amincewar rinjayen ‘yan Majalisar ta dattawa, kuma ya tsallake mataki na biyu.
Ziyarar ta Harry na kwana uku domin halartar bukukuwan cika shekara 10 da kadamar da wasannin 'Invictus Games' na sojojin da aka raunata a fagen daga.
Kungiyoyin fararren hula da masana shari’a a Najeeriya sun fara jan hankalin gwamnati cewa kada ta yarda a yi tsarin sasantawa a wajen kotu ko kuma "Plea Bargain" a turanc, wato ba da wani kason kudin da ake zargi don a rufe batun.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce da sanyin safiyar Juma’a Yarima Harry zai gana da Babban Hafsan Hafsoshin rundunar tsaron Najeriya, Janaral Christopher Gwabin Musa.
Sanarwar da ta musanta zargin, wanda mai magana da yawun Ministan Yada Labarai, Rabi'u Ibrahim ya sa hannu, ta ce bita da kulli ne kawai, kuma kage kamfanin ya yi wa gwamnatin ko kuma jami'anta.
Domin Kari
No media source currently available
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.
Kungiyar ta Transparency International ta ce matsalar cin hanci a bangaren shari’a ya na ci gaba da yin mummunar illa ga marasa galihu. A game da girman wannan matsala, mun tattauna da Auwal Musa Rafsanjani, Daraktan kungiyar ta Transparency International a Najeriya.