Gwamnatin rikon kwarya ta Jamhuriyar Nijar ta maida martani bayan da shugaban kasar Benin Patrice Talon ya dauki matakin hana lodin danyen man da Nijar ke shirin fara shigarwa kasuwannin duniya a tsakiyar watan Mayu.
Akalla mutum 90 aka samu tabbacin sun ji raunuka iri-iri a N’djamena, babban birnin kasar.
Alkaluman zaben sun nuna cewa Deby Itno ya samu kashi 61 cikin 100 na kuri’un da aka kada, yayin da Masra ya samu kashi 18.5 cikin 100.
Alkaluman zaben sun nuna cewa Deby Itno ya samu kashi 61 cikin 100 na kuri’un da aka kada, yayin da Masra ya samu kashi 18.5.
A cewar rahoton, adadin mutanen da zasu fuskanci matsalar karancin abinci a yankunan yammaci da tsakiyar nahiyar afirka a wannan dan tsakani zai kai kimanin mutane milyan 52 kwatankwacin kaso 12 cikin 100 na mutanen da aka tantance.
A ranar Juma’a ne likitoci a Kenya za su koma bakin aikin su, bayan sun amince da gwamnatin a kan yadda za a biya su sauran albashinsu da ya makale.
Shugaban kasar Kenya William Ruto ya ayyana Juma'a a matsayin ranar hutu domin makokin mutane 238 da suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa da ake ci gaba da yi.
An kiyasta cewa ana samun asarar dala tiriliyan 3.6 a tattalin arzikin duniya a shekara, a sanadiyar harkokin da suka danganci cin hanci da rashawa.
Shugaban na Senegal ya zabi a shiga filin jirgin saman ba tare da wani kace-nace ba. Ba wani jerin gaishe-gaishe ko wani biki. Da ga shi sai abokan tafiyar sa kawai.
Gwamnatin ta dauki wannan matakin ne na rufe wuraren hakar ma’adinan zinare dake arewacin kasar bayan da wasu dabbobi suka mutu sakamakon shan ruwa mai dauke da guba a wurin.
A watan Mayu ne ya kamata a fara jigilar danyen man Nijar daga tashar jirgin ruwan Seme a jamhuriyar Benin zuwa kasuwannin duniya, gwamnatin shugaba Patrice Talon ta yanke shawarar hana gudanar da wadannan ayyuka da nufin maida martani ga mahukuntan Nijar da ke ci gaba da rufe iyakar kasar.
Domin Kari
No media source currently available
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.
Kungiyar ta Transparency International ta ce matsalar cin hanci a bangaren shari’a ya na ci gaba da yin mummunar illa ga marasa galihu. A game da girman wannan matsala, mun tattauna da Auwal Musa Rafsanjani, Daraktan kungiyar ta Transparency International a Najeriya.