Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ZABEN 2015: APC Ta yi Galaba a Bauchi da Gombe


Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda
Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda

Sakamakon zaben Bauchi da Gombe ya nuna APC ta yi galaba.

Sakamakon zaben jihohin Bauchi da Gombe sun nuna jam'iyyar APC ta yi rawar gani.

A jihar Bauchi APC ta lashe duk kujerun majalisar dattawa guda ukun kana ta lashe na jamalisar wakilai goma sha biyu.

Malam Aliyu Abubakar kakakin hukumar zabe yace APC ce ta lashe zaben Bauchi.A zaben shugaban kasa APC ta samu kuriu fiye da dubu dari tara yayinda PDP ta samu dubu tamanin da shida da 'yan kai.

A jihar Gombe ma tsohon gwamnan Danjuma Goje ya lashe kujerar sanata a karkashi APC. Usman Nafada ya lashe kujerar sanata a Gombe ta tsakiya. Sanata Lidani ma ya sake samun komawa.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:42 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG