Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rahoto na Musamman a Kan Boko Haram: Jini, Hawaye da Fargaba a Daular El-Kanemi


Tashin bam da ya kashe mutane akalla 15 a sananniyar kasuwar nan da ake kira Monday Market a Maiduguri ranar 1 Yuli, 2014, na daya daga cikin tashe-tashen bama bamai da suka addabi yankin arewacin Najeriya. (AFP)
Tashin bam da ya kashe mutane akalla 15 a sananniyar kasuwar nan da ake kira Monday Market a Maiduguri ranar 1 Yuli, 2014, na daya daga cikin tashe-tashen bama bamai da suka addabi yankin arewacin Najeriya. (AFP)

Kashe-kashe da zub da jini da tashe-tashen hankula sun zamo ruwan dare a yankin arewa maso gabashin Najeriya a dalilin hare-haren ‘yan Boko Haram.

Kashe-kashe da zub da jini da tashe-tashen hankula sun zamo ruwan dare a yankin arewa maso gabashin Najeriya a dalilin hare-haren ‘yan Boko Haram. A yayin da wannan tashin hankali ke bazuwa zuwa wasu sassan na Najeriya, har ma da makwabtanta, fargaba tana kara yawaita cewa watakila gwamnatin Najeriya ba ta san yadda zata takali wannan batu ba. Ko kuma tana kara rura wutar fitinar ne ma da kanta.

A daidai lokacin da aka fara ganin soja na farko ya sa wuka zai yanka mutum na farko a hoton bidiyon nan, akwai gawar mutum guda cikin ramin da aka tona, da kuma jini a bakin ramin daga inda aka yanka shi. A bayansu, akwai mutanen dake zaune a layi kafin a zo kansu.

Karin Bayani akan Jini, Hawaye da Fargaba a Daular El-Kanemi >>

XS
SM
MD
LG