Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Ta Samu Zababbiyar Gwamnar Jaha Mace Ta Farko


This photo shows participants crossing the Jiaozhou Bay Bridge as they compete in the 2017 Qingdao International Marathon on the Sea in Qingdao in China's eastern Shandong province.
This photo shows participants crossing the Jiaozhou Bay Bridge as they compete in the 2017 Qingdao International Marathon on the Sea in Qingdao in China's eastern Shandong province.

An yi abin tarihi a Najeriya. An samu zababbiyar gwamnar jaha mace ta farko.

A wani al'amari na tarihi, Najeriya ta samu zababbiyar gwamnar jaha mace ta farko, wadda ba ma daga kudancin kasar ta fito ba; daga arewacin kasar ta fito - inda ada ake ganin hakan da matukar wuya.

Wannan al'amarin, wanda rahotanni ke nuna cewa ya faranta wa jama'a da dama - musamman ma mata da matasa da sauran ma'abuta canji - rai, ya biyo bayan hukuncin da Kotun Daukaka kara ta Tarayya da ke babban birnin Tarayyar Najeriya Abuja ta yanke dazu-dazun nan, inda ta ayyana Sanata A'isha Jummai Alhassan a matsayin Gwamnar jahar Taraba.

Ga wakilanmu Hassan Maina Kaina da Ibrahim Abdul'aziz daga Abuja da Taraba da cikakkun rahotannin:

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:37 0:00
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:09 0:00

XS
SM
MD
LG