A cikin hira da wakilinmu na jihar Bauchi, mataimakin shugaban kungiyar har ila yau yace daga yanzu kungiyar zata daina kai hari kan jami'an tsaro, ta kuma bukaci ganin suma jami'an tsaro su daina kai hare hare kan al'umma.
Kungiyar Boko Haram tace daga yanzu ta daina kaiwa jami'an tsaro hari ta kuma nemi suma a daina kai masu hare hare
Mataimakin shugaban kungiyar Jamatu Lidda awati Ahli suunati wal Jihad wadda aka ba lakabi da sunan Boko Haram, Muhammad Marwana ya bayyana cewa kungiyar ta saki turawa yan kasar faransi guda bakwai da suka saka yi garkuwa da su na tsawon watanni biyu sabili da sa baki da kuma roko da al'ummar musulmi sukayi tayi a kafofin yada labarai da kuma nuna alamar zahiri dangane da batun neman sasantawa da gwamanatin Najeriya take nema.
A cikin hira da wakilinmu na jihar Bauchi, mataimakin shugaban kungiyar har ila yau yace daga yanzu kungiyar zata daina kai hari kan jami'an tsaro, ta kuma bukaci ganin suma jami'an tsaro su daina kai hare hare kan al'umma.
A cikin hira da wakilinmu na jihar Bauchi, mataimakin shugaban kungiyar har ila yau yace daga yanzu kungiyar zata daina kai hari kan jami'an tsaro, ta kuma bukaci ganin suma jami'an tsaro su daina kai hare hare kan al'umma.