Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Boko Haram Tayi Alkawarin Daina Kaiwa Jami'an Tsaro Hari


Wakilan kungiyar Boko Haram ta Najeriya wadda Amurka ke yin gargadi game da yiwuwar wani harin da za ta kai kan manyan otel-otel din da Turawa ke sauka a Abuja.
Wakilan kungiyar Boko Haram ta Najeriya wadda Amurka ke yin gargadi game da yiwuwar wani harin da za ta kai kan manyan otel-otel din da Turawa ke sauka a Abuja.

Kungiyar Boko Haram tace daga yanzu ta daina kaiwa jami'an tsaro hari ta kuma nemi suma a daina kai masu hare hare

Mataimakin shugaban kungiyar Jamatu Lidda awati Ahli suunati wal Jihad wadda aka ba lakabi da sunan Boko Haram, Muhammad Marwana ya bayyana cewa kungiyar ta saki turawa yan kasar faransi guda bakwai da suka saka yi garkuwa da su na tsawon watanni biyu sabili da sa baki da kuma roko da al'ummar musulmi sukayi tayi a kafofin yada labarai da kuma nuna alamar zahiri dangane da batun neman sasantawa da gwamanatin Najeriya take nema.

A cikin hira da wakilinmu na jihar Bauchi, mataimakin shugaban kungiyar har ila yau yace daga yanzu kungiyar zata daina kai hari kan jami'an tsaro, ta kuma bukaci ganin suma jami'an tsaro su daina kai hare hare kan al'umma.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:15 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG