Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Alhamis cewa barazanar da Amurka ta yi na hana makamai ba za ta hana Isra’ila ci gaba da kai hare-hare Gaza ba, lamarin da ke nuni da cewa za ta iya yin gaban kanta wajen mamaye birnin Rafah mai cunkoson jama’a ba tare da goyon bayan babbar kawarta ba
Shugaban kasar Kenya William Ruto ya ayyana Juma'a a matsayin ranar hutu domin makokin mutane 238 da suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa da ake ci gaba da yi.
Shugaba Joe Biden ya fada jiya Laraba cewa ba zai aika da muggan makamai ga Isra'ila da za ta iya amfani da su wajen kai hare-haren wuce gona da iri kan Rafah ba, wanda yake tungar karshe ta Hamas a Gaza, saboda nuna damuwa kan yadda zai afka kan fararen hula fiye da miliyan 1 da ke fakewa a wurin.
Hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya ta umarci kamfanin samar da wutar lantarki da ya rage yawan wutar da ake ba abokan hulda a kasashen ketare domin bunkasa samar da wutar lantarki a cikin gida.
Kungiyar mayaka ta Falasdinu a jiya Litinin ta amince da shawarar tsagaita bude wuta a Gaza daga masu shiga tsakani, sai dai Isra'ila ta ce sharuddan ba su biya bukatunta ba, kuma za ta ci gaba da kai hare-hare a Rafah yayin da take shirin ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar.
Bakin haure akalla 107 da suka hada da mata da yara da ke garkame ne aka kubutar a wani gari da ke kudu maso gabashin kasar Libya, kamar yadda wani mai magana da yawun hukumar tsaron kasar ya sanar a ranar Litinin.
Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Dallas na kasar Amurka, domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron kasuwanci na Amurka da Afirka na 2024 wanda kungiyar kamfanoni kan Afirka ta shirya.
Isra'ila ta ba da umarnin rufe ofisoshin gidan talabijin na Aljazeera na Qatar da ke kasar a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya kara dagula takaddamar da ke tsakanin tashar watsa labaran da gwamnatin Firaminista Benjamin Netanyahu.
Amurka za ta bayar da kusan dala miliyan 55 don magance matsalar jin-kai a Burkina Faso, in ji jami’ar bayar da agaji ta Amurka Samantha Power a ranar Alhamis, a cewar wata sanarwa da Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya gani.
Wata kungiyar 'yan tawaye da ake zargin tana da alaka da kasar Rwanda ta kwace garin Rubaya da ke gabashin kasar Congo inda ake hakar ma'adanai a gabashin kasar da ya shahara wajen samar da wani muhimmin ma'adinan da ake amfani da su a wayoyin salula na zamani, a cewar kungiyar a ranar Alhamis.
Wani jami'in Amurka ya fada a ranar Alhamis cewa Rasha ta tura wasu sojojinta zuwa wani sansanin sojin sama a Jamhuriyar Nijar inda wasu 'yan tsirarun sojojin Amurka suka rage bayan da akasarin sojojin Amurka suka fice daga sansanin da ke Yamai babban birnin kasar.
An gudanar da gasar lig ta wasan kwallon Kwando da Olympics ta musamman ta nahiyar Afirka a Dakar, babban birnin kasar Senegal, da wasu rahotanni
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya bayyana a ranar Laraba cewa, Turkiyya za ta bi sahun Afirka ta Kudu wajen shigar da kara kan kisan kiyashin da Isra'ila ke yi a kotun kasa da kasa (ICJ).
Gwamnan Jihar Ebonyi a Najeriya, Francis Nwifuru, ya sake bayar da karin Naira 10,000 ga albashin ma’aikatan jihar.
Domin Kari