Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Aware Sun Kashe 11 a Indiya


​Hukumomin jahar Assam ta arewa maso gabashin kasar Indiya sun ce 'yan awaren wata kabila sun kashe mutane 11.

Sau biyu aka kai hare-hare da yammacin jiya Alhamis a lokacin da mutane ke gidajen su su na bacci.

'Yan sanda sun ce 'yan tawaye mayakan haramtacciyar kungiyar National Democratic Front of Bodoland ne suka bude wuta a gundumar Kokrajhar, suka kashe mutane 8. Kuma suka kashe wasu mutum uku a cikin wani hari na daban da suka kai gundumar Baksa. Aka ce wadanda aka kashen Musulmi ne.

Wannan tashin hankali ya wakana ne cikin matsanantan matakan tsaro a Assam a daidai lokacin da ake zaben 'yan majalisar dokoki a kasar Indiya wanda za a yi makonni biyar ana yi.

An dade ana fama da kiyayya da zargin satar filaye a Assam tsakanin 'yan kabilar Bodo da kuma dubban 'yan kabilar Bengali Musulmi, wadanda da yawan su zuwa suka yi daga yankin gabashin Pakistan kafin ya zama Bangladesh a shekarar Alif dari tara da saba'in da Daya (1971).

A shekarar 2012 ma fadan kabilancin da aka yi a wannan yanki na jahar Assam, yayi sanadiyar mutuwar mutane 100 a kalla, kuma ya tarwatsa wasu mutanen fiye da dubu 400.

A arewa maso gabashin kasar Indiya kungiyar National Democratic Front of Bodoland na daya daga cikin dimbin kungiyoyin 'yan tawayen da ke yakin neman warewa suka kafa kasar su, su kadai.
XS
SM
MD
LG