Masana da kwararru sunyi nazarin cewa kungiyar Habaka Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ko CEDEAO, na bukatar sake tsari da sauye-sauyen da za su yi daidai da manufofin kasashe mambobinta.
Gwamnatin mulkin soji a Burkina Faso ta kori wasu jami'an diflomasiyyar Faransa uku bisa zarginsu da yin zagon kasa, kamar yadda wata takarda da gwamnati ta wallafa a shafukan sada zumunta ta ce ranar Alhamis.
Shugaban Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya yi wa fursunoni sama da 4,000 afuwa, ciki har da wasu da ke jiran hukuncin kisa, a wata afuwar zagayowar ranar bikin ‘yancin kai a ranar Alhamis.
Jirgin mai saukar ungulu na dauke ne da mutum 11 ciki har da Janar Ogolla a lokacin da ya fado kasa ya kama da wuta a kusa da kan iyakar kasar da Uganda.
Kungiyoyin siyasa guda 9, a kasar Ghana, sun hada kawance don tsayawa takara a babban zaben kasa mai zuwa da za a gudanar a Disambar 2024.
An cimma wata yarjejeniyar da a karkashinta jamhuriyar Nijar ta amince ta sayar wa kasar Mali lita million 150 na man diesel akan farashi mai sauki.
Shugaban kasar Mali ya sanar a jiya Talata cewa, kasar Nijar za ta kai lita miliyan 150 na dizal domin samar da wutar lantarki a makwabciyar kasa ta Mali a daidai lokacin da kasar ta yammacin Afirka ke fama da matsalar rashin wutar lantarki.
Hukumomin gundumar Caia sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, kwale-kwalen na dauke da mutane 12 galibi manoma.
Kungiyar kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta ce ana sa ran wata tawaga za ta isa Togo a cikin wannan mako, yayin da tashe-tashen hankula ke kara ta’azzara game da sake fasalin tsarin mulkin kasar da 'yan adawa suka ce zai tsawaita wa'adin mulkin shugaba Faure Gnassingbe.
Hukumar Kwastam ta Senegal ta ce ta kwato fiye da tan guda na hodar ibilis a kudu maso gabashin kasar, inda ta bayyana shi a matsayin kamu mafi girma da aka taba yi na jigilar hodar iblis a kan hanyar kasa a yammacin Afirka.
Gwamnatin rikon kwaryar jamhuriyar Nijar ta sanar da karbar bashin dalar Amurka million 400 daga kamfanin man fetur CNPC na kasar China, domin daukan dawainiyar wasu daga cikin mahimman ayyukan kasa.
Manyan jami'an diflomasiyya da kungiyoyin agaji sun yi taro ranar Litinin a birnin Paris, domin bullo da hanyoyi na taimakon jin kai ga kasar Sudan da ke arewa maso gabashin Afirka, wadda ke daf da fuskantar matsananciyar yunwa, domin gudun sake fadawa cikin mawuyacin hali.
Domin Kari
No media source currently available