Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yajin Aikin Ma’aikata a Ghana


Shugaban Kasar Ghana John Dramani Mahama.
Shugaban Kasar Ghana John Dramani Mahama.

Ministan daukar ma’aikata da harkokin kwadago Haruna Idrisu ya bayyana al’ajabinsa akan matakin da aikatan kasar Ghana suka dauka yana cewa, “a madadin gwamnati ina nuna matukar al’ajabina da nadama ga wannan matakin da ma’aikata suka dauka.

dalili kuwa shine a daidai lokacin da ma’aikatan suke bayyana shawararsu na wannan yajin aiki lokacin kenan dasuka kaura cewa gayyata da gwamnati tabasu don tattaunawa akan bukatunsu.”

Ministan dai yace mun basu wannan gayyata tun daga ranar sha hudu zuwa sha shida gawannan watan na Oktoba, amma dai sai ya cigaba yana cewa, “ina tabbatar wa ‘yan Ghana musammanma ma’aikatan Ghana, cewa kudinsu na fansho yana nan babu abinda ya same shi, saidai bamu yarda da tsarin kulawa da hatsarin ke tattare da ladan ‘yan fanshon ma’aikatan neba.”

Shi kuma shugaban kungiyar malumman Christian Ada Ikpoku yace gwamnatin batabi yadda yakamataba shiyasa basu halarci gayyata da gwamnati tabasu ba, yakuma kara da cewa yakamata a shirya zaman da Kyau ba’a zafi wasu a zauna dasu abar saura ba. Saikuma shugaban ma’aikatan kananan hukumomi shikuma Izik Banfo yace “naga alama gwamnati bata bin doka kuma ta kwan da sani cewa majalisar dokokice ta shirya wannan doka don haka dole gwamnati ta kula da kudaden ‘yan fansho.

Yawancin mutane dai basu da labarin wannan yajin aikin, makarantu nanan na aiki to saidai kuma wasu babu malumai, Asibitoci da dama musamman ma na Akara suna nan na aikinsu.

Gwamnatin dai na bin kungiyoyin kwadago kan a zauna warware wannan matsala.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:30 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG