Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsaron Kasa Aikin Kowa Ne, Inji Daliban Arewa Maso Gabashin Najeriya


'yan gangamin neman a kubutar da daliban da aka sace a Najeriya
'yan gangamin neman a kubutar da daliban da aka sace a Najeriya

Tallafawa ya zama wajibi inji hadakar daliban shiyyar arewa maso gabashin Najeriya tun da dalibai ake kashewa, kuma su aka hana yin karatu

Hadakar kungiyoyin daliban shiyyar arewa maso gabashin Najeriya ta ce matsalolin tsaron da suka addabi jahohin shiyyar sun fi karfin a tsurawa hukuma idanu a bar ta ita kadai.

A kan haka ne hadakar kungiyoyin daliban ta gudanar da wani taro a Jalingo, babban birnin jahar Taraba.

Cikin takaici, da nuna damuwa daliban su ka kudiri aniyar bayar da ta su gudunmowa. Daliban su ka ce idan ana so a shawo kan wannan bala'i dole sai an hada kai, sai an hada karfi da karfe.

Comrade Mohamed Auwal Jibril shi ne shugaban hadakar kungiyoyin dalibai a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:48 0:00
Shiga Kai Tsaye

Wakilin Sashen Hausa na Muryar Amurka a jahohin Adamawa da Taraba, Ibrahim Abdulaziz ne ya hada wannan rahoto.

XS
SM
MD
LG