Kwamitin sulhun ya kuma sabunta aikin kiyaye zaman lafiya da Majalisar ke yi a kasar na tsawon shekara daya.
Majalisar Dinkin Duniya ta kakabawa kasar takunkumin ne a shekarar dubu biyu da hudu bayan yakin basasar da aka yi a kasar daga shekara ta dubu biyu da biyu zuwa shekara ta dubu biyu da uku.
Kudurin da aka amince dashi bai daya a kwamitin , ya kuma yi maraba da shawarwarin da ake yi tsakanin jam'iyyun siyasar kasar da kuma ingantuwar kare hakki da 'yancin jama'a a kasar.
Yanzu haka akwai sojojin kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya dubu shida da dari tara a kasar ta Ivory Coast.
To sai dai jam'iyyun masu hamayya da kungiyoyin kare hakkin jama'a a kasar sun yi Allah wadai da kudurin na Majalisar Dinkin Duniya.