Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mace Tayi Kunar Bakin Wake a Maiduguri


ႏိုင္ငံျခားေရးဝန္ႀကီးဌာန ျပည္ေထာင္စုဝန္ႀကီး ေဒၚေအာင္ဆန္းစုၾကည္ႏွင့္ အေမရိကန္ျပည္ေထာင္စု ႏိုင္ငံျခားေရးဝန္ႀကီး ဂၽြန္ကယ္ရီ တို႔ေတြ႔ဆံု
ႏိုင္ငံျခားေရးဝန္ႀကီးဌာန ျပည္ေထာင္စုဝန္ႀကီး ေဒၚေအာင္ဆန္းစုၾကည္ႏွင့္ အေမရိကန္ျပည္ေထာင္စု ႏိုင္ငံျခားေရးဝန္ႀကီး ဂၽြန္ကယ္ရီ တို႔ေတြ႔ဆံု

Talatannan ne wata mace ta kai harin kunar bakin wake a birnin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya.

Talatannan ne wata mace ta kai harin kunar bakin wake a birnin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya.

Misalin karfe 11 na rana da mintuna 20 ne aka samu tashin wasu tagwayen boma-bomai wadanda ake zaton wata mace ce ta kaishi a bayan kasuwa da ake cewa Monday Market.

Rahotanni da Sashen Hausa na Muryar Amurka yake samu na cewa wannan hari yayi sanadiyar rayuka a kalla 30, da dama kuma sun jikkata.

Bayanai dake fitowa daga asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri na cewa an kai gawarwaki fiye da talatin da wani abu.

A kwanakin baya dai, an fuskanci cewa ana yin amfani da mata wajen kai hare-hare, musamman tun bayan sace dalibai mata yara sama da 200 daga makarantarsu ta sakandare dake Chibok.

‘Yan jarida a birnin Maiduguri sun bayanna cewa jama’a sun san mayakan Boko Haram, lamarin dake kalubalantarsu wajen kai hare-haren bom a cikin birnin, shiyasa suke amfani da mata.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG