Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kakakin Majalisar Wakilan Nigeria ya Karbi Takardun Tsayawa Takarar Gwamnan


Alhaji Aminu Waziri Tambuwal. Kakakin Majalisar wakilan Nigeria.
Alhaji Aminu Waziri Tambuwal. Kakakin Majalisar wakilan Nigeria.

Kakakin Majalisar wakilan Nigeria Ahaji Aminu Waziri Tambuwal yace ya karbi takardun neman tsayawa takarar gwamnan jihar Sokoto karkashin jam'iyar APC, bayan ya tuntunbi shugabani da kuma musamma yan jihar Sokoto.

Kakakin Majalisar wakilan Nigeria Aminu Waziri Tambuwal ya karbi takardun neman tsayawa takarar gwaman jihar Sokoto, karkashin jam'iyar APC.

Daukan wannan mataki da kakakin yayi ya kawar da jita jitan da aka yi ta yayatawa na rashin alkibilar kakakin Majalisar, wanda kwanaki baya ya karbi takardun neman tsayawa takarar shugaban kasar.

Yace sai da yayi shawarar da shugabani na kasa da jama'a musamman na jihar Sokoto akan cewa dawowa akan matsayin tsayawa takarar gwamnan shine a'ala.

Dalili ke nan daya sa kakakin ya yanke wannan hukunci ko shawara.

Ga karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:39 0:00

XS
SM
MD
LG