Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Taraba ta Tashi Haikan Akan Habbaka Ayyukan Noma


Gwamnan Jihar Taraba, Danbaba Suntai
Gwamnan Jihar Taraba, Danbaba Suntai

Mukaddashin gwamnan jihar Taraba Alhaji Umar Garba ya bayyana irin hobasar da jihar keyi wurin habbaka ayyukan noma da nufin rage kudin da kasar ke kashewa wurin shigo da cimaka kamar shinkafa.

Wani bature dake sarafa shinkafa a kasar Kenya ya je kihar Taraba an kuma bashi kadada dubu talatin domin ya noma shinkafa ya kuma sarafata a kamfanin da zai kafa jikin jihar.

Mukaddashin gwamnan yace idan Allah ya yadda nan da shekara daya ko biyu jihar Taraba zata samar da kashi 15 cikin dari na adadin shinkafar da kasar ke ci kuma take sayowa daga waje.

Na biyu gwamnati ta baiwa Dangote kadada dubu arba'in da biyar domin ya shuka kara na yin sukari a nan jihar. Sukarin da zai yi zai fi na kamfaninsa na yanzu. Yaran jihar zasu samu su shiga cikin aikin.

Mutanen da suka bayar da filayensu za'a basu iri da zasu shuka. Wato an samu riba kashi biyu ke nan. 'Ya'yan wadanda suka bayar da filaye za'a basu aiki a kamfanin su ma iyayen za'a basu iri su shuka. Kamfanin kuma zai sayi kayansu da suka shuka.

Har yanzu jihar tana da fili da take son ta bayar. Duk wanda yake bukatar fadada aikin gona ya nufi jihar a bashi fili.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:41 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG