Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Allah Ya Yiwa Ahmad Chalabi Rasuwa


Ahmed Chalabi
Ahmed Chalabi

Dan siyasar da ake zargi da taimakawa wajen ingiza mamayar da Amurka ta yiwa kasar Iraqi a shekarar 2003, Ahmad Chalabi ya rasu a yau Talata

‘Yan majalisu da kafar yada labaran kasar sun ce Chalabi ya rasu ne a birnin Bagadaza yana mai shekaru 71, yayin da ya ke rike da mukamin shugaban kwamitin da ke kula da kudade a majalisar dokokin kasar.

Ya kwashe mafi yawan rayuwarsa ne a kasar Birtaniya da Amurka, inda ya samu digiri na biyu da kuma digirin digirgir.

Mutane da dama na alakanta zamansa a Amurka da mamaye Iraqi da Amurka ta yi, wanda ya yi sanadin hambarar da gwamnatin Saddam Hussein.

Mr. Chalabi shi ne wanda ya baiwa Amurka bayanan sirrin cewa Iraqi na da makaman kare-dangi, sai dai kimarsa ta fadi a idon mutane da dama bayan da aka gano Iraqin ba ta da makaman.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG